ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Bidiyon shahararren dan kwalo sanda yake wanke bahayan masallaci

Lamarin ya faru sa'o'i kadan bayan dan kwallon ya taimaki kungiyar sa wajen doke abokan adawar su a wasan gasar firemiya da aka buga ranar asabar.

Masallacin mai suna Al-rahman dake nan titin Mulgrave a birnin Liverpool na kasar Ingila nan ne dan wasan yake gabatar da sallolin sa.

Wasan da Liverpool tayi da kungiyar Leicester wanda aka tashi 2-1, dan kasar Senegal ya zura kwallo daya a raga wanda ya taimaki kungiyar sa wajen samun galaba a kan abokan adawar su.

ADVERTISEMENT

An haifi Mane ne a cikin addinin musulunci, kuma ya girma a garin Bambali dake kudancin kasar Senegal inda mahaifinsa ne limamin masallacin garin, hakan ya sanya shi mutumi mai riko da addini.

Dan wasan mai shekaru 26 a duniya yana daya daga cikin fitattun yan wasan kwallon kafa dake alfahari da addinin su. Yakan yi sujududa don nuna godiya idan yayi nasarar zura kwallo a raga.

Dan kwallo yana daya daga cikin yan wasa da ake jin duriyar su a duniyar kwallon kafa ta duniya a halin yanzu.

Yayi nasara lashe gwarzon dan wasan watan Agusta ta gasar firemiya sakamakon rawar da ya taka ma Liverpool a watan.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT