Hukumar yan sanda na jihar Katsina sun cafke wani magidanci mai shekaru 46 yana jima’i da akuya a bayan gidan sa.
An kama wani magidanci mai yara 6 yana jima’i da akuya
Yan sanda sun kama wani magidanci mai matsananciyar yunwar jima’i yana jima’i da akuya a jihar Katsina
Wanda ake zargi Babangida Garba mazaunin kasuan mata dake karamar hukumar Funtua na cikin jihar Katsina. Matar sa tare da taimaƙon yan anguwa suka kai karar shi ga hukumar yan sanda yayin da matar shi ta cafke shi yana aikata wannan mumunar aiki.
Garba yace bai san abun daya tunzura shi yin haka kuma har da laifin matar sa don ta hana shi jima’i tunda ta dauki ciki.
Ya furtar cewa wannan shine karo na biyu da yake aikata wannan aikin, kuma yana rokon huƙumar yan sanda, al’ummar sa da iyalensa da su yafe mai kuma ba zai kara aikata laifin ba.
Wamishnar yan sanda na jihar Katsina Aliyu Abdullahi, yace za’a kai karar shi kotu bisa ga zargin yin jima’i da wata jinsin halirta.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng