ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

An kama yan bindiga 20 tare da makamai

Kwamishnan yace ba za'a sanar da wuraren da aka kama su kuma hukumar baza ta sanar da sunayen su ba bisa ga wasu dalilai na tsaro.

Kwanmishnan yan sanda ta jihar Kenneth Ebrimson ya sanar da haka yayin da ya zanta da manema labarai a garin Gusau ranar Laraba 15 ga watan Agusta.

Yace dakaru ta musamman daga ofishin shugaban yan sandan Nijeriya tare da hadin gwiwar sauran jami'ai dake sassa daban-daban suka yi nasara kama yan bindigar.

Ya kara da cewa bisa ga tsatsaurar mataki da rundunar ta dauka wajen fatattaki yan bindigar akwai yiuwar samun galaba cikin yan kwanakin nan.

ADVERTISEMENT

A bisa bayanin sa, rundunar ta kaddamar da dakaru masu sintiri domin rage tashin hankali da cece-kuce dake yaduwa game da tsaro tare da kama wadanda ke haifar da tarzoma.

Daga karshe ya shawarci al'ummar jiha da su taimaki jami'an tsaro da duk wata labari da zai taimaka wajen kawoi karshen ta'adanci ko sace-sace a jihar.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT