ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

An gano sandar majalisa dokoki

Sanarwar ta kara da cewa an jefar da sandar ne sakamakon matakin tsaurara tsaro da jami'an rundunar yan sanda suka yi a Abuja

Yan daba sun far ma zauren majalisa ranar laraba 18 ga wata yayin da yan zauren ke gudanar da zama kamar yadda ta saba har suka saci sandar majalisa.

Kamar yadda mataimakin jami'in hulda da jama'a na rundunar SP Aremu Adeniran ya sanar, an gano sandan a daidai yankin city Gate dake nan garin Abuja.

Sanarwar ta kara da cewa an jefar da sandar ne sakamakon matakin tsaurara tsaro da jami'an rundunar yan sanda suka yi a Abuja.

Sakamakon hargitsin da ya faru a zauren majalisar yan sanda sun kama Sanata Ovie Omo-Agege wanda ake zargi da kawo yan dabar zauren har suka sace sanda.

ADVERTISEMENT

Shima mataimakin shugaban majalisar Ike Ekwerammadu wanda ya jagoranci zaman a bisa rashin shugaban sa wanda yayi tafiya domin halartar taro a Amurka, ya kai ziyara fadar shugaban kasa inda ya kora ma mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo bayanai kan abun da ya faru a zauren majalisa.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT