ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Za'a nada Adam Zango da sarautar 'Sarkin Kannywood' bisa ga wasu dalilai

Kungiyar ta bayyana dalilain da ya sanya zasu nada jarumin da sarautar bayan tattaunawa da suka yi tsakanin su

Falla M Sherrif wanda yake shine shugaba mai riko na kungiyar ya zanta wa jaridar RARIYA cewa kungiyar zata nada jarumin da sarautar bayan tattaunawa da tayi kan wanda yafi cancanta.

Ya bayyana dalilai da yasa zasu ba Adam Zango sarauta kamar haka : "Don kasancewar sa mai hakuri, iliminsa mutuncinsa, kyautarsa, biyayyarsa, ibadarsa, yafiyarsa ida an yi masa laifi da kuma daukakarsa. Sannan kuma mawaki ne, makadi ne,furodusa ne, darakta ne, edita ne, jarumi ne, dan rawa ne da dai sauransu.

Shugaban kungiyar ya kuma kara da cewa, yanci da masu kallo ke dashi a wajen masu shirya fina-finai yana daga  cikin dalilin nada shi saboda a dalilin su ake shirye fina-finan hausa domin su siya.

Al'amarin ya janyo farin cikin ga dinbim masoyan jarumin 'Gwaska" inda suka gudanar da biki na taya murnar samun wannan sarauta.

ADVERTISEMENT

Sai dai wannan sabon sarauta zai raba hankalin jama'a ya kuma sanya alamar tambaya ga masu bibiyan masana'antar Kannywood.

Sanin jama'a ne cewa an nada jarumi Ali Nuhu da wannan sarautar kuma mafi yawanci ma dashi aka yi masa lakabi.

A wata sako da ya wallafa a shafin sa na Instagram kwanan baya, jarumi Bello Muhammed Bello yayi kira na a gudanar da zabe domin nada sarautar Sarkin kannywood domin bada hanyar zaben wanda yafi cancanta.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT