ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Anyi tashe-tashen bama-bamai a garin maiduguri

Rahoto ya nuna cewa bam huɗu suka fashe lokaci guda yayin da guda biyu suka kara fashewa bayan minti 15

an samu fashewar bama-bamai

An samu fashewar bama-bamai a garin maiduguri a daren ranar talata 18 ga watan yuli

A labarin da kamfanin dilancin labarai (NAN) suka fitar, fashewar sun faru tsakanin karfe 10:45 da 11 na dare a babban birnin jihar Borno.

Rahoto ya nuna cewa bam hudu suka fashe lokaci guda yayin da guda biyu suka kara fashewa bayan minti 15.

Wannan ya faru bayan farmakin da wata yar kunar bakin wake ta kai a masallaci wanda ya kashe mutum 12 a safiyar ranar litinin.

ADVERTISEMENT

Mun samu labari cewa karfin girgijen bama-bamai da suka fashe ya cire rufin gidajen mutane dake garin

Babu tabbatacciyar labari game da illar da fashewar ya haifa.

Amma dai NAN sun kawo rahoto cewa rundunar sojoji sun harbi wasu da suke zargi da yan boko haram wadanda ke neman kai farmaki a garin wanda sakamaƙon harbin ya haifar da jerin fashewar bama-bamai.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT