Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya jajanta ma iyalin dan majalisar dattawa kuma tsohon gwamnan jihar Gombe Danjuma Goje bisa ga rasuwar uwargidan sa Hajiya Yelwa Goje.
Shugaba Muhammadu Buhari yayi ma Sanata jaje game da mutuwar matarsa
Shugaban yace hakika mutuwar uwa yana ma ginshikin gida barazana domin irin ayyukan da take yi ga iyalin ta
A sakon ta'aziya da kakakin shugaban Garba Shehu ya fitar ranar Litinin, shugaba Buhari yace mutuwar hajiya Yelwa ya razanar dashi.
Shugaban yace hakika mutuwar uwa yana ma ginshikin gida barazana domin irin ayyukan da take yi ga iyalin ta wajen kula da yara da kuma faranta ran su.
Daga karse shugaban ya ma Sanata Goje da iyalen shi addu'a na Allah ya basu hakurin jure wannan babban reshi kuma Allah ya jikan ta da Rahama.
Hajiya Yelwa Goje ta rasu a asibiti dake ƙasar Amurka bayan wata ciwo da take fama da ita.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng