ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Aisha Buhari tayi kira ga mata da su koyi sana’a domin dogaro da kansu

Uwargidan tafadi haka a wata takarda da kakakin ta Suleiman Haruna ya fitar ma manema labarai ranar laraba a garin Abuja

Uwargidan shugaban ƙasa Aisha Buhari tayi kira ga mata dake ƙasar da su koyi sana’a domin taimakon kansu da daukar dawainiyar gidajen su.

Uwargidan tafadi haka a wata takarda da kakakin ta Suleiman Haruna ya fitar ma manema labarai ranar laraba a garin Abuja.

Bisa ga takardar matar shugaban ƙasa ta fadi haka ne a garin Bauchi yayin ƙaddamar da wani shiri wanda zai yi wa mata 1,000 horo akan sana’o’i daban daban.

Shirin dai yana daya daga cikin tsare-tsaren Aisha Buhari domin taimaka ma yan ƙasa.

ADVERTISEMENT

A bikin wanda matar gwamnan jihar Bauchi Hajiya Hadiza Abubakar ta wakilce ta, Aisha Buhari tace dole mata su zage damtse a matsayin su na iyaye wajen koyan sana’a.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT