Uwargidan shugaban ƙasa Aisha Buhari tayi kira ga mata dake ƙasar da su koyi sana’a domin taimakon kansu da daukar dawainiyar gidajen su.
Aisha Buhari tayi kira ga mata da su koyi sana’a domin dogaro da kansu
Uwargidan tafadi haka a wata takarda da kakakin ta Suleiman Haruna ya fitar ma manema labarai ranar laraba a garin Abuja
Uwargidan tafadi haka a wata takarda da kakakin ta Suleiman Haruna ya fitar ma manema labarai ranar laraba a garin Abuja.
Bisa ga takardar matar shugaban ƙasa ta fadi haka ne a garin Bauchi yayin ƙaddamar da wani shiri wanda zai yi wa mata 1,000 horo akan sana’o’i daban daban.
Shirin dai yana daya daga cikin tsare-tsaren Aisha Buhari domin taimaka ma yan ƙasa.
A bikin wanda matar gwamnan jihar Bauchi Hajiya Hadiza Abubakar ta wakilce ta, Aisha Buhari tace dole mata su zage damtse a matsayin su na iyaye wajen koyan sana’a.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng