ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Haya-gaga a zauren majalisar dokoki yayin da wani dan majalisar ke neman sauya sheka zuwa APC

Dan majalisar ya sanar cewa bisa ga wasu dalilai na rashin gamsarwa dake wakana a cikin jam'iyar PDP na jihar tashi har ma da ta kasa baki daya ya sanya zai barta zuwa jam'iyar adawa.

A zaman da yan majalisar suka yi ranar laraba 17 ga watan yau, sanata Sonny Ogbuoji mai wakiltar jihar Ebonyi ya tashi tsaye a zauren domin sanar cewa ya sauya sheka daga PDP zuwa APC.

Wannan sanarwar bata yi ma sauran yan jam'iyar PDP dadi ba inda suka nemi shi da ya dakatar da yin haka har sai ya shawarci yan jam'iyar.

Bisa ga wannan yunkurin suma yan APC dake zauren suka bukaci shi da ya cigaba da aniyar sa.

ADVERTISEMENT

Bayan mintuna 15 da yin nazari dan majalisar ya dakatar da sanarwar tashi har sai bayan ya tuntubi yan jam'iyar PDP.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT