Mutum 18 sun mutu yayin da 29 suka jikata a harin da ya faru a garin Muna Gari dake karamaar hukumar Konduga na jihar Borno yammacin ranar laraba.
Yan kunar bakin wake sun kai hari masallaci da gidajen yan gudun hijira
Mutum 18 sun mutu yayin da 29 suka jikata a harin da ya faru gidan yan gudun hijira dake wajen garin Maiduguri
Kakakin hukumar yan sanda na jihar mista Victor Isuku ya tabbatar da harin a wata takarda da ya fitar ma manema labarai a garin Maiduguri.
Kakakin yace lamarin ya faru daidai karfe 6:30 na yamma yayin da wasu yan kunar bakin wake hudu suka kai harin garin dauraye da bama-bamai a jikin su.
A bisa bayanin sa, tashin bam na farko ya faru ne cikin masallaci kuma daga bisani sauran suka tashi a wurare daban-daban na yankin.
Isuku yace wadanda suka ji rauni sanadiyar harin suna samun kulawa a asibitin koyi na jami'ar maiduguri tare da asibitocin gwamnati na jihar.
Daga karshe kakakin ya sanar da cewa an tura wasu runduna zuwa garin domin kawar da tashin hankali a zukatan mazaunin garin.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng