ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Yan kunar bakin wake sun kai hari masallaci da gidajen yan gudun hijira

Mutum 18 sun mutu yayin da 29 suka jikata a harin da ya faru gidan yan gudun hijira dake wajen garin Maiduguri

Mutum 18 sun mutu yayin da 29 suka jikata a harin da ya faru  a garin Muna Gari dake karamaar hukumar Konduga na jihar Borno yammacin ranar laraba.

Kakakin hukumar yan sanda na jihar mista Victor Isuku ya tabbatar da harin a wata takarda da ya fitar ma manema labarai a garin Maiduguri.

Kakakin yace lamarin ya faru daidai karfe 6:30 na yamma yayin da wasu yan kunar bakin wake hudu suka kai harin garin dauraye da bama-bamai a jikin su.

A bisa bayanin sa, tashin bam na farko ya faru ne cikin masallaci kuma daga bisani sauran suka tashi a wurare daban-daban na yankin.

ADVERTISEMENT

Isuku yace wadanda suka ji rauni sanadiyar harin suna samun kulawa a asibitin koyi na jami'ar maiduguri tare da asibitocin gwamnati na jihar.

Daga karshe kakakin ya sanar da cewa an tura wasu runduna zuwa garin domin kawar da tashin hankali a zukatan mazaunin garin.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT