ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Buhari ya iso London lamin lafiya - inji kakin sa

Adesina yace Buhari ya iso London bayan ya halarci taron koli na majalisar dinkin duniya a New york

Shugaba Muhammadu Buhari ya iso birnin London bayan ya halarci taron koli na majalisar dinkin duniya da aka yi a New york ranar alhamis 21 ga watan Satumba.

Kakakin shugaban kasar Femi Adesina ya bayyanar da isowar shi London.

Adesina yace Buhari ya iso London bayan ya halarci taron koli na majalisar dinkin duniya a New york cikin lamin lafiya.

“Tafiyar shugaban kasa na sati daya kuma tun ranar lahadi yayi tafiyar kuma ranar lahadi ko litinin zai dawo. Duk da cewa ya tafi London  shugaban ba zai wuce yadda ya kayyade” yace.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa bai sanar da dalilin da yasa shugaban ya tafi London Adeshina ya bayyana ma gidan talabijin na Channels cewa shugaban ba zai wuce yadda ya kayyade ba.

Yayin da yake kasar Amurka wajen taron koli na majalisar dinkin duniya shugaba Buhari ya jawabi akan abubuwa dake faruwa a Nijeriya da ma duniyar baki daya. Kafin ya bar Amurka yaci abincn rana tare da shugaban kasar Donald Trump.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT