ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

An nemi shaida an rasa, kotu da dage ranar saurara karar taqaddamar Maryam Sanda

James Idachaba ya shaida ma kotu cewa ya halarci dakin tare da masu bada shaida su hudu sai dai daga baya an nemi daya daga cikin su an rasa

Anyi zaman ne a ranar litinin 19 ga wata kuma daga bisani alkalin ita wanda ake zargi da laifi ya shaida ma mai shari'a cewa babban shaida da ya kamata a fara tambayoyi a kan shi yayi tafiyar iska domin an nemi shi an rasa.

Alkalin wanda ake tuhuma kan laifin kisa James Idachaba ya shaida ma kotu cewa ya halarci dakin tare da masu bada shaida su hudu sai dai daga baya an nemi daya daga cikin su an rasa.

Sauran shaidun da aka gabatar a kotun sun hada da Maimuna Sanda (mahaifiyar Maryam), Aliyu Sanda (Dan uwan ta) da Sadiya Aliyu (Yar aikin gida).

Ana zargin su da sa hannu wajen kashe Bilyaminu Bello dan tsohon shugaban jam'iyar PDP wanda ya rasu a gidan sa dake garin Abuja

ADVERTISEMENT

Mai shari'a Halilu Yusuf ya daga ranar saurara karar zuwa ranar 19 da 20 ga watan Afrilu.

Sai dai alkali mai bada kariya Joseph Daudu ya nemi kotu da ta yi watsi da buktar da alkalin maryam ya nema na a laifin kisa da aka shigar.

A zaman kotu da aka yi a ranar 7 ga watan maris, mai shari'a Halilu Yusuf ya bata damar yin beli domin halartar zaman kotu daga gida bisa rokon da alkalin ta yayi sakamakon barazanar lafiyar jiki da take fuskanta sanadiyar juna biyu da take dauke dashi.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT