Shaharariya ‘yar wasan kwaikwayo Rahama Sadau ta bayyana cewa korar da ƙungiyar MOPPAN na masana'antar Kannywood tayi mata ya bude mata kofofin samun nasara tare da karin masoya.
Dakatarwa da aka yi mun ya bude mun kofofin samun nasara
Rahama tace mutane da dama da basu santa a da suna goyon bayan ta yanzu
Fittaciyar jarumar ta ayana haka a wata hira ta musamman da tayi da jaridar Guardian lifestyle.
Game da dalilin da yasa aka kore ta tauraruwan tace;
Rahama tace hakika ba ko wani matsayi da aka bata tayi take karba indai matsayin ya saɓawa addinin ko al’adar ta.
Haifiyar jihar Kaduna ta kara da cewa ta watsi da wani matsayyi da aka bata na kwaikwayan yan madigo don ya saɓawa addinin ta.
Kusan shekara daya kenan da ta samun korar daga masana’antar Kannywood bayan ta rungumi mawaki Classiq a cikin wani bidiyon wakar shi.
Yar wasan ƙwaikwayon tace wannan ya bude mata kofofin samun nasara tunda yanzu har ta fara fitowa a shirin fina-finan masana’antar Nollywood da dama tare da wasu nasarori.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng