ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Maryam Sanda ta nemi a sake ta ta hanyar beli kan wata sabuwar dalili

Alkalin ya nemi kotu da ta bayar da damar beli ga Maryam bisa cikin da take dauke dashi wanda ya kai na tsawon wata uku

Ana tuhumar ta kan zargin kashe mijinta Bilyaminu Bello dan tsohon shugaban jam'iyar PDPBello Halliru a gidan su dake nan garin Abuja.

Wakilin ta Joseph Daudu ya sanar da haka a gaban kotu ranar litinin yayin da ake sauraron karar ta.

Alkalin ya nemi kotu da ta bayar da damar beli ga Maryam bisa cikin da take dauke dashi wanda ya kai na tsawon wata uku.

Kasancewa an daure Maryam a gidan kaso kuma daga nan take ziyartar dakin kara,  alkalin yaroki kotu da ta ba maryam damar cigaba da halartar kotu kan karar ta daga gida ba domin kula da juna biyun da take dauke dashi.

ADVERTISEMENT

Joseph Daudu ya sha alwashin bayanar da ita a duk sanda ake zaman kotu kan karar ta domin yanke mata hukuncin laifin da ake zargin ta da aikatawa.

Shi dai alkalin wanda ya shigar da kara kotu James Idachaba yace sun shigar da kara don ayi watsi da bukatar da alkalin Maryam ya roka.

Mai shari'a Yusuf Halilu ya daga ranar sauraro zuwa 7 ga watan yau domin zartar da hukunci kan bukatar da ta nema.

Laifin Maryam Sanda

Maryam ta daba ma tsohon mijinta marigayi Bilyaminu Bello wuka cikin watan nuwamba na bara. Sanadiyar laifin da ta aikata ake ta kai-kawo wajen zantar da hukuncin laifin ta.

ADVERTISEMENT

Auren ta da marigayi an samu diya mace yar wata takwas.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT