ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Majalisa ta bukaci Buhari ya bayyana gaban ta kan kashe-kashen dake faruwa

Ta bukaci shugaban da ya gabatar da kanshi zauren domin bada bayanin matsalar tsaro da ake fuskanta a kasar

Majalisar tayi wannan kiran ne a zaman majalisa da tayi yau laraba 25 ga watan Afrilu.

Ta bukaci shugaban da ya gabatar da kanshi zauren domin bada bayanin matsalar tsaro da ake fuskanta a kasar.

Sai dai majalisar bata sanar da ainihin ranar da shugaban zai bayyana a gaban ta. Yan majalisar sun kuma gudanar da zaben kin jin bisa gazawan jami'o'in tsaro na kasa wajen kawo karshen kashe-kashen dake faruwa a kasa.

Wannan matakin dai ya biyo bayan kudirin da Mark Gbillah, dan majalisa mai wakiltar jihar Benue ya shigar, kan kashe-kashen da ya faru a jihar sa.

ADVERTISEMENT

Bayan muhawara da su kayi kan kudirin yan majalisar suka yanke shawarar gayyatar shugaban kasa.

Yan majalisar dai sun dangata rikicin dake faruwa a kasar ga gazawan shugaban kasa wajen kalubalantar jami'o'in tsaro wajen inganta aikin su.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT