Wasu daga cikin yan majalisar dokoki sunyi tsokaci game da kasafin kudin shekara 2018 da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gabatar a zauren ranar talata.
Yan majalisar dokoki sunyi tsokaci game da kasafin kudi da shugaba Buhari ya gabatar
Sanata Adamu Abdullahi yace akwai walakin goro a miya dangane da kasafin kuma za'a samu nasara idan an bi hanyar da ya kamata
Wasu daga cikin su sun jinjina wa shugaban yayin da wasu kuma yi akasarin haka.
Hirar sa da kamfani dake dilancin labarai ta NAN, sanata Abdullahi Adamu yace akwai walakin goro a miya dangane da kasafin kuma za'a samu nasara idan bi hanyar da ya kamata.
Hakazalika shima sanata Ovie Omo-Agege (APC daga jihar Delta) ya jinjiwa shugaban kasa tare da yin ikirari na cewa ya shirya bunkasa ayyuka a kasar har zuwa lokacin da shugabancin shi zai kare.
Dan majalisan ya yabawa shugaban game da kasafin kudin tare da yin la'akari ga kudin da aka ware ga ma'aikatar bunkasa yankin neja delta ta NDDC.
Omo-agege yace shugaba Buhari ya sauke nauyin dake kansa da doka ta kafa yanzu nauyin ya koma ga yan majalisa.
Shi kuma sanata Peter Nwaboshi (PDP daga jihar Delta) ya jinjinawa shugaban dangane da jajircewan sa da yawan lokaci ya dauka wajen yin jawabi amma yayi korafi game da jawabin domin ya sa rai cewa shugaban zai dogara da irin nasarori da aka samu a yankin neja delta.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng