ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Buhari ya rattaba hannu ga dokar bada fifiko ga yan kasa fiye da yan kasar waje wajen bayar da kwangilar aiki.

Shugaban ya sa hannu ga wannan dokar jiya litinin 5 ga watan janairu a fadar sa dake nan Abuja.

"A cikin wannan doka ta shugaban kasa, Shugaban ya ba da umarni ga hukumomi da ma'aikatun gwamnati su rika bayar da fifiko ga kamfanonin cikin gida wajen tsarawa da aiwatar da ayyukan tsaron kasa". kamar yadda fadar shugaban kasa ta wallafa a shafinta na Twitter.

Shugaban yace an dauki wannan matakin ne domin samad da aikin yi ga yan kasa.

Shugaban ya haramtawa ma'aikatar cikin gida bayar da bisa ga 'yan kasashen wajen da za su shigo Najeriya domin gudanar da dukkan ayyukan da akwai wadanda ka iya yin su a kasar.

ADVERTISEMENT

Sai dai shugaban yace dai, a inda ba' a samu yan kasa kwararu za' a iya bayar da kwangilar ga kamfanonin kasar waje.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT