Bisa labari da majiya suka shaida mana, SARS tayi awon gaba da dan majalisar cikin karfin iko zuwa ofishin su dake nan kusa da tsohon ofishin babban bankin Nijeriya dake nan Abuja, inda za'a tsare shi domin amsa tambayoyin zargin da ake masa.
Jami'an SARS sun cika hannu da dan majalisa
Lamarin ya faru bayan sanarwa da Dino Melaye yayi na mika wuya domin bada amsar tambayoyi kan zargin da ake masa
Lamarin ya faru ne bayan sanarwa da Dino Melaye yayi na mika wuya domin bada amsar tambayoyi kan zargin da ake masa.
Tun cikin watan Maris rundunar yan sanda suka kaddamar dashi a matsayin wanda take nema ruwa a jallo bayan tsammaci da suka tura mai na zuwa ofishin su wajen bada amsar tambayoyin zargin da wasu yan tawaye da makami suka yi masa.
Yan tawayen, Kabiru Saidu da Nuhu Salihu sun bada amasa cewa dan majalisar ya daukin nauyin su wajen hadasa rikici a jihar Kogi yayin da zaben 2019 ke yunkurowa.
Sunyi wannan shaidar ne yayin da jami'an tsaro suka kama su a garin Ogojueje na karamar hukumar Dakina na jihar.
Sai dai sanatan ya ki amincewa da amsa gayyatar da aka yi masa, ya nisantar da kanshi ga zargin da ake masa. A cewar shi yan sanda da gwamnatin jihar Kogi sun hada kai wajen ci masa fuska.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng