Shugaban majalisar gwamnonin yankin arewa Gwamna Kashim Shetima na jihar Borno yace hakika shugabannin na da rawa da zasu taka wajen tabbatar da zamn lafiya tsakanin yan ƙasa a duk inda suke.
Gwamnonin arewa sun ziyarci kudancin Nijeriya
Wannan yana cikin shirin kawar da rikicin kabila dake neman kunno wuta tsakanin hausawa da yan kabilar Ibo
Gwamnan ya fadi haka ranar litinin 18 ga watan Satumba 2017 yayin da tawagar gwamnonin arewa suka ziyarci gwamnan jihar Abiya Ikeazie Ikpeazu a gidan gwamnati dake Umuahia.
Yace ya zama wajibi akan ko wani shugabannin na tabbatar da zaman lafiya a ko ina kuma kundin tsarin mulkin ƙasa ta ba ko wani ɗan ƙasa damar zama a duk inda ya ga dama indai bai sabawa wa dokar kasa.
Gwamnonin sun yaba ma gwamnan jihar Abia bisa ga yadda ya bida zaman ɗarɗar da ya faru a jihar kwanan baya.
Gwamna Ikpeazu yayi wa gwamnonin godiya har ya kara da cewa zai tabbatar cewa duk wani ɗan ƙasa dake karkashin shugabancin ya samu yanci kamar ko wani dan ƙasa ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.
Majalisar gwamnonin sun kai ziyara ga gwamnan jihar Ribas Nyesom Wike shima a fadar gwamnati dake Port harcourt.
Cikin jerin ziyara da yasamu goyon bayan Shugaba Muhammadu Buhari gwamnonin zasu ziyarci sauran jihohin yankin kudancin ƙasar kana su koma jihohin su.
cikin tawagar gwamnonin akwai gwamnan jihar Sokoto, Kebbi, Filato, Katsina da Borno.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng