ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Gobara a farfajiyar majalisar dattawa, yan majalisa sun tsere da gudu

A wani dakin aikin dake ginin ya kama da wuta a safiyar ranar alhamis 15 ga wata yayin da dattawan ke kai-kawo a zauren

Gobara ta kama a wani sashe na farfajiyar majalisar dattawa wanda ya sanya wasu yan majalisar tserewa domin kubita daga inda wuta ke ci.

A wani dakin aikin dake ginin ya kama da wuta a safiyar ranar alhamis 15 ga wata yayin da dattawan ke kai-kawo a zauren su.

Gobarar ta faru ne sanadiyar lalacewar na'urar bada iska dake daidai dakin kula da ayyuka na bangaren majalisar dattawa  na zauren yan majalisun Nijeriya.

Ma'aikata da baki sun tsere don neman tsira har zuwa ga lokacin da jami'an zauren suka samu damar kashe gobarar.

ADVERTISEMENT

Jim kadan bayan faruwar haka, dan majalisa Abdullahi Gobir yayi koken cewa zauren bata kai ga zaman inda yan majalisa zasu zauna.

Sakamakon gobarar da ya faru shugaban majalisar Bukola Saraki ya daga ranar zaman yan majalisar zuwa ranar talata 20 ga wata 2018 inda za'a daura daga inda aka tsaya.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT