ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Gwamna yayi barazanar fitar da hotuna 11 masu razanarwa game da halin rashin lafiyar Buhari

Fayose yace babu gaskiya cikin bayanin da Osinbajo ya fitar na cewa Shugaban kasa na murmurewa

President Muhammadu Buhari

Gwamnan jihar Ekiti Ayo Fayose ya fito yana cewa ya mallaki wasu hotuna wanda zai razanar da ‘yan kasa game da halin rashin lafiyan shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Gwamnan ya kara da cewa bayanin da mukaddashin shugaban kasa ya fitar na cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari na murmurewa karya ce wanda bata da tushe.

Mukaddashin shugaban Yemi Osinbajo wanda yaje kasar Britanniya don gana da shugaban ranar talata ya bayana ma manema labarai ranar laraba bayan dawowarsa cewa shugaban na murmurewa kuma nan ba da jimawa zai dawo kasar.

Lokacin da ya gana da manema labarai a garin Abuja ranar laraba 12 ga watan Yuli Fayose ya kara jaddada cewa gara shugaban kasa yayi murabus don neman magani ma  rashin lafiya da yake fama da ita.

ADVERTISEMENT

“In ba ayi hankali zan bayyanar da wasu hotuna wanda na san in na fitar da su zasu razanar da ‘yan nijeria. A gaskiya offishin gwamnoni da na shugaban kasa na bukatar ayyuka. In ba a yi hankali ba zan fitar da hotuna 11 wanda ke nuna halin da shugaban ke cikin.” gwamnan ya furtar.

Gwamnan dai yace ba wai yana mummunar fatan ma Buhari.

Ya yi inkari da Osinbajo inda yace mukaddashin ya fitar da hoto ko bidiyo na ganawar da ya yi ranar talata a bainar ‘yan kasa. Gwamnan ya kara da cewa Osinbajo ya fadi hakikanin gaskiyar abun da ya gani game da rashin lafiyar shugaban

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT