Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar cewa baza ta lamunta da ayyukan wasu mabiyan kungiyoyi daya sabawa doka ba ko kuma yake gurbatar da zaman lafiya dake jihar.
Gwamnatin jihar Kaduna tayi kashedi ga yan darikar shi'a kan yi wa zaman lafiya barazana
Gwamnati tace zata kama duk wanda ya fito zanga-zanga a jihar karkashin kungiyar Islamic movement of Nigeria
A wata takarda da ta fitar ranar litinin wanda kakakin gwamna Samuel Aruwan ya sa hannu, gwamnatin jihar ta fitar da wannan kashedi bayan lamarin da ya faru a jihar Kano kwanan baya tsakanin yan mazhabar shi'a da jami'an tsaro.
Aruwan ya kara da cewa gwamnati ta sanar da jami'an tsaro wajen kawar da duk wani aiki dake neman kawo barazana akan zaman lafiya a jihar.
A baya gwamna yace Akwai zaman lafiya a jihar Kaduna kuma mun ɗau matakai na kare mutane da dukiyoyin su
Kakakin ya sanar cewa gwamnati baza ta amince da duk wani aikin kungiya wanda doka bata san da ita a jihar kuma yayi kira ga jama'a da su kai karar duk wani kungiya dake neman gurbatar da zaman lafiya ga jami'an tsaro.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng