Rundunar yan sanda dake jihar Kano ta kama wasu gawurtaccen masu garkuwa da yara a garin Kano kana sun kubitar da yara 7.
An kubitar da yara 7 tare da kama wasu matasa 3 masu garkuwa da yara kanana a garin Kano
Yayin da suka kama masu garkuwan, jami'an sun samu damar kubitar da yara bakwai daga maboyar da suka aje su.
Bisa ga rahoton da muka samu wannan lamarin ya faru ne ranar alhamis 16 ga watan Nuwamba a garin Kano.
Jami'in hulda da jama'a na hukumar yan sanda DSP Magaji Musa Majia ya tabbatar da kamun masu laifin masu suna kamar haka: Khalifa Usman wanda aka yi wa lakanin Gurgun Layin Pole na kurna da Idris Aminu daga Lokon Sheshe Quarters Kano da Abdullahi Aminu wanda aka fi sani da Sharu na Sharifai Quarters.
Dsp Magaji yace hanyar da suke amfani dashi wajen tafiyar da barnar da suke shine, idan sun kama yara daga birni sai su tafi dasu kauyukan wasu kananan hukumomin kamar Dambata da Gwarzo Da Gezawa inda zasu mika su ga mai unguwar kauyen a matsayin yaran da suka tsinta a hanya kana su bukaci iyayen yaran da su tura masu katin waya kafin su samu yaran su.
Labari ya nuna cewa sun samu katin waya wanda ya wuce N100,000 daga iyayen yara.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng