ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Buhari zai gana da Trump, ga abubuwan da zasu tattauna akai

Shugaba Muhammadu Buhari zai kai ziyara kasar Amurka 30 ga watan afrilu inda zai tattauna kan wasu muhimman batutuwa da shugaba Donald Trump

A wata takardar sanarwa da sakataren watsa labarai na fadar shugaban Amurka ta White house,  Sarah Huckabee Sanders ta sanar cewa shugaban Amurka zai gana shugaban Nijeriya ranar 30 ga watan afrilu  a fadar sa.

Kamar yadda sanarwar ta bayyana, shugabannin zasu tattauna kan batutuwa da ya hada da, hanyoyin kawo sauyi kan harkar kasuwanci da yaki da ta'adanci da kuma hanyar ingantar lamura a Nijeriya ta yadda zata cigaba da zama jagorar dimokradiya a nahiyar Afrika.

Sakataren ta kara da cewa akwai kyakywar alaka tsakanin kasar Amurka da Nijriya.

Wannan ba shi bane haduwar su na farko tunda shugaba Buhari ya hau kujerar mulki, a cikin watan Satumba na shekarar 2017 shugabannnin sun hadu a taron karrama wasu shugabannin kasashen afrika da majalisar dinkin duniya ta hada.

ADVERTISEMENT

Ziyara zuwa kasar Ingila

Yanzu haka shugaba Buhari Buhari yana kasar Ingila inda ya kai ziyarar aiki tun ranar 9 ga watan yanzu.

Shugaban zai gana da firayin ministan Ingila Theresa May kan dangantaka dake tsakanin kasar Nijeriya da Ingila.

Shugaban zai kuma tattauna da shugaban kamfanin Dutch royal plc mista Ben van Beurden da kamfanin Shell da makamantan su kan matakin zuba jari a masana'antar mai na kasar Nijeriya.

Daga karshe shugaban zai gana da wasu jami'ai na Ingila da kuma yan Nijeriya mazaunin kasar.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT