ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Ko dai shugaba Buhari ya fara yakin neman zabe?

Hotunan fosta sun fara yawo a titunan garin Abuja

Hotunan fosta na yaki neman zabe na shugaba Muhammadu Buhari ya fara yawo a sassa na garin Abuja.

A rahoton da jaridar Premium Times ta fitar, an gano hotunan mai dauke da fuskar Shugaba Buhari tare da mataimakin shi Yemi Osinbajo a titunan garin Abuja.

" A madadin matasan Neja Delta da matan yankin da kuma kungiyar tsaro dake goyon bayan Buhari/Osinbajo muna goyon bayan zarcewar ka a zaben 2019" rubutun dake cikin fostar kenan tare da hoton wani Felix Ubokan a matsayin wanda ya dauki nauyin wallafawa.

Duk da cewa har yanzu shugaban bai tsayar da maganar fitowa takara a zaben 2019 akwai alama shugaban zai bayyana kuddirin sa nan gaba.

ADVERTISEMENT

kwanan baya yayin da yake ganawa da yan Nijeriya mazaunin kasar Cote D'ivoire, shugaban yace ya ziyarci wajen taron ne tare da wasu gwamnoni biyu domin yin haka zai taimaka wajen yakin neman zabe nan gaba.

Hakazalika yayin da ziyarci jihar Kano kwanan baya shugaban yayi tsokaci game da dimbin mutane da suka tarbe shi inda yake cewa " ina cike da farin ciki ganin dimbin jama'a da suka tarbe ni, da wannan na san idan aka gudanar da zabe a halin yanzu hakika zan ci nasara."

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT