Ƙaramar Ƙungiyar PDP dake ƙarƙashin shugabancin Ahmed Makarfiya yi iƙirarin cewa ƙaramar ƙungiya dake cikin APC ta amshi Mulki saboda rashin lafiyar Shugaba.
Jam'iyya ta ce ƙaramar ƙungiya da ke cikin ƙungiyar APC ta amshi mulki daga shugaban ƙasa
PDP ta yi wannan tsokacin saboda rashin kasancewar Shuagaba a taro na sati-sati na FEC so uku a Wata ɗaya.
Kakakin PDP, Prince Dayo Adeyeye a wani sanarwa ya ce, Rashin kasancewar Buhari a taron FEC ya nuna Cewa Kasar na bisa "jirgin dake tuka kansa"
Muna jaje da Shugaba akan lafiyarsa, kuma muna addu'a Allah ya sai mai hannuwansa, yanzu an tabbatar cewa ƙasa na a ƙarƙashin jagorancin ƴan ƙungiyar dake cikin ƙungiyarsu, ba a san mambobin ƙungiyar ba.” Adeyeye ya ce.
Wa ke lura da ƙasar yanzu? ba mu sani ba. Najeriya a yanzu na bisa jirgi dake tuƙa kansa, ba mu san mai lura da ƙasar ba da kuma mai ba da umurni ko mai amfani da ƙarfin ikon shugaba ba.
“Wannan ba zai iya faruwa a wurare inda da hankali, mu na da Shugaba da bamu gani ba a fili yan kwanakin nan ba, kuma Gwamnati ba ta nuna damuwa ba." ya ƙara cewa
Duk da haka, Ministan Bayanai, Lai Mohammed ya ce rashin kasancewar Buhari ba sabon abu bane.
A cewar Mohammed, Buhari ya riga ya ce bai taɓa irin wannan rashin lafiyar a duk rayuwarsa ba, saboda haka ya nuna a fili ƙalubalen lafiyarsa.
Buhari ya yi wannan tsokacin bayan ya dawo Najeriya daga hutu na kwana 49 na duba lafiyarsa a ƙasar London.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng