ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Shekau ya fitar da sako a cikin faifan bidiyo (Bidiyo)

Yace kungiyar tana nan lafiya kuma babu jami'an tsaro da zasu hana sukaurace daga bakan su

Wannan shine karo na farko da shugaban kungiyar zai fitar da sako ga jama'a bayan ya kwashi kwanaki da dama bai yi hakan ba.

A cikin sakon da ya fitar, Shekau yana tabbatar ma jama'a cewa wannan sakon gaisuwa ne kuma suna nan lafiya babu abun da ya same su.

Jagoran boko haram ya kara da cewa babu abun da jami'an tsaro zasu iya tsinana masu kuma babu abun da zasu samu daga gare su domin suna cikin inuwar Allah. Bugu da kari yana mai sanar ma jami'an  tsaro cewa babu mutumin da zai koma ga Allah sai dai idan har kwanan sa ya kare.

ADVERTISEMENT

Har ila yau dai Shekau yana mai ikirarin cewa suna suka gabatar da hare-hare da ya faru kwanan baya a garin Maiduguri da Damboa har da Gamboru.

Har ila yau dai an rasa samun maboyar kungiyar.

A kwanan baya wani tsohon kwamandar kungiyar ya sanar cewa Shekau ya tsere dutsen Mandara domin tsira daga jami'an tsaro dake yaki da kungiyar.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT