Hukumar dake yaki da masu yima kasa zagon kasa ta EFCC ta kama tsohon sakataren gwamnati tarayya Anyim Pius Anyim.
Hukumar EFCC ta kama tsohon sakataren gwamnatin tarayya
Rahotannin sun nuna cewa Anyim yana karban horo mai tsanani daga jami'an hukumar
Bisa ga labarin da jaridar Sahara reporters ta fitar, an kama shine bisa ga zargin badakalar kwangilar gina garin Abuja centinery City.
A cikin watan maris na 2017 kwamitin majalisar dokokin kan lamuran birnin tarrayya tayi kira na a tuhume tsohon sakataren gwamnatin tarayya da tsohon ministan Abuja sanata Bala Muhammed bisa ga yin almundahana da kwangilar.
A kwanann baya ma kungiyar yan kabilar Ibomazaunin kasashen waje tayi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari da yayi bincike akan batun Anyim Pius Anyim.
Rahotannin sun nuna cewa Anyim yana karban horo mai tsanani daga jami'an hukumar.
Takaitaccen tarihin Sa
Anyim Pius Anyim shine sakataren gwamnatin tarayya a zamanin mulkin tsohon shugaban kasa Goodluck Ebele Jonathan.
Kafin ya zama sakataren gwamnati, ya kasance dan majalisar dattawa mai wakiltar jihar Ebonyi karkashin jam'iyar adawa ta PDP.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng