ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

An cafke wasu masu safarar miyagun kwayoyi a filin jirgin sama na Aminu kano

Yace dai an kama su ne yayin da ake binciken bayan saukar su daga jirgin sama

Babban kwamandar hukumar na filin jirgin mista Ambrose Umoru ya sanar da haka yayin da ya bayyanar da masu laifin su biyu ga manema labarai ranar alhamis 1 ga watan Maris.

Yace dai an kama su ne yayin da ake binciken bayan saukar jirgi.

Daya daga cikin masu laifi wanda asali da dan karamar hukumar Indemili South dake jihar Anambra ne ya shiga hannu jami'an hukumar bayan na'urar bincike ta bayyana wasu kwayoyi wadanda ya hadiye wanda ake tsammani cewa ta kai kilo 2.180.

Mai laifin wanda ke sana'ar aski a kasar jamhoriyar Congo ya shigo kasar ne da kwayoyin daga kasar Burundi kuma yana kokarin safarar kwayoyin zuwa jihar Anambra dubun sa ya cika.

ADVERTISEMENT

Dayan mai laifin mace, yar shekara 32 kuma yar asalin jihar Delta ta shigo da fararen gari wanda ake tunanin cewa garin iblis ne ta shigo dasu ne daga kasar Habasha.

Umaro yace matasan Nijeriya sun tsallake rijiya da kafar dama inda yayi la'akari da illar da kwayoyin zasu haifa idan sun samu nasarar shiga dasu kasar.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT