ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Hisba ta kama almajirai 65 a jihar kano

Muhammed yace an kama su ne a yankuna daban daban nan garin Kano cikin watan Nuwamba sanadiyar yawon kame-kame da jami'an hukumar tayi

Ma'aikacin hukumar wanda ke sashen kawar da barace-barace malam Dahiru Muhammed ya shaida wa manema labaran kamfanin dillancin labarai ta NAN haka a garin Kano ranar talata.

Muhammed yace an kama su ne a yankuna daban daban nan garin Kano cikin watan Nuwamba sanadiyar yawon kame-kame da jami'an hukumar tayi kana ya kara da cewa cikin mutum 65 da suka kama 8 yara kana ne , sauran mutum 57 balagaggu ne.

A bisa bayanin sa mutum 47 daga cikin su yan asalin jihar Kano ne amma sauran mutum 18 sun hada da yan jihar Bauchi, Jigawa, Gombe, Kogi da Zamfara.

ADVERTISEMENT

Hukumar ta sake wasu daga cikin su kasancewa wannan shine karo na farko da suka aikata haka.

Daga karshe Muhammed yace wadanda yan asalin jihohin dake makwabtaka da jihar Kano ne an mayar dasu jihohin su.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT