Rundunar yan sanda na jihar Kaduna ta tabbatar cewa a ranar lahadi aka direkta wanda ke aiki a ma’aikatan karatu na jihar ya samu yanci daga wadanda suka yi garkuwa dashi.
An saki direkta wanda aka yi garkuwa dashi
Rundunar yan sanda na jihar ta tabbatar cewa direkta wanda aka saki a safiyar ranar lahadi ya koma ga iyalin shi
Kakakin yan sanda ASP Mukhtar Aliyu ya tabbatar da haka ranar lahadi yayin da ya gana da manema labarai na NAN.
Ya bayyana cewa direktan wanda aka saki safiyar ranar lahadi ya koma ga iyalin shi.
Aliyu ya sanar cewa wata mata mai shayarwa wanda aka saci tare da direktan ta samu yanci itama.
Kakakin bai sanar ko akwai fansa da aka biya don su samu yanci daga wadanda suka sace su.
Aliyu yayi kira ga yan jihar da su cigaba da taimakon jami’an tsaro wajen bada labari da zai taimaka masu wajen magance ire-iren miyagun ayyuka da aukuwa a jihar da ma kasar baki daya.
Kamfanin dillancin labarai (NAN) ta ruwaito cewa an saci John Gorah a tsakar daren ranar 3 na watan Satumba a gidansa dake Mararaban rido na jihar Kaduna.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng