Ciƙin tsarin maganta cin hanci da rashawa da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ta ƙirƙiro, ya tabbata cewa “Yan fasa-tulu” na cin moriyar tsarin.
Gwamnatin tarayya ta biya "yan fasa tulu" 20 miliyan N375.8
Ministan ƙudi Kemi Adeosun ta bayyana haka inda tace wannan shine biyan farƙo da gwamnati ta fara yi cikin tsarin “Yan fasa-tulu”.
Mutum 20 suka taimaka wajen samun miliyan N11.6 kuma cikin tsarin ko wanne cikin su na da kashi biyar cikin kudin da suka taimaka aka gano.
Ministan kudi Kemi Adeosun ta bayyana cewa miliyan N375.8 aka kasa tsaƙanin wanda suka taimaka.
Wannan na nuna cewa tsarin na aiki kuma ta cika alaƙwarin da ta dauka game da tsarin.
Duk da cewa babu wani masaniya game da labarin ko wanne da zai ci moriyar aikin da yayi.
Ministan bayyana cewa an ƙirƙiro wannan tsari don magance cin hanci da rashawa dan ita ke gurɓatar da kasar tun ba yau ba kuma gwamnatin mu zata cigaba da neman hanya wajen ƙashe wannan mumunnan hali.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng