ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Gwamna yá dakatar da ʼƴan jarida biyu daga yin rahoto akan ayyukan Gwamnati

Al-makura bai ji daɗin yadda ʼƴan jarida biyu sun yi rahoto a kan wasu shuwagabanin ƙungiyar ƙwadago wanda aka kashe.

___5806162___https:______static.pulse.com.gh___webservice___escenic___binary___5806162___2016___11___24___16___tanko-Al-Makura

An dakatar da Umar Muhammad na Gidan Jaridan Punch da Rabiu Omaku na Gidan Jaridan Universal Reporters wanda yake yanar gizo, daga yin rahoto a kan ayyukan Gwamnatin Jihar Nasarawa.

Muna da rahoto cewa akwai saɓani tsakanin Mashawarcin Gwamna akan harkokin watsa labarai- Ahmed Tukur da Muhammad.

'Ƴan jarida wanda gwamnati ta dakatar da su a jihar Nasarawa, sun zama biyar.

ADVERTISEMENT

Shugaban masu rahoto na Jihar Nasarawa, Mr Suleiman Abubakar ya yi wannan sanarwa cewa Gwamnatin Nasarawa ta hana Muhammed da Omaku daga yin rahoto.

Abubakar ya ce:

“Mashawarcin Gwamna Al-Makura  a kan harkokin watsa labaru ya ce an dakatar da ku biyu (Muhammed da Omaku) har abada abadin, daga yin rahoto a kan ayukkan gidan gwamnati da ayyukan gwamnatin Nasarawa gaba ɗaya. Ya ce wannan umarni daga wurin maigidansa ne.”

Sauran ʼƴan jarida wanda aka dakatar da su daga yin rahoto game da ayyukan Gwamnatin Nasarawa su ne; Mary Amirikpa na Gidan Labarai na Jihar Nasarawa, Iliya Audu na Nigerian Newsday, da Sofia Ogaze na Television Continental.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT