Gwamanatin jihar kano ta bada hutun ƙwana daya ranar talata 4 ga watan Yuli 2017 don jan’izar Maitama Sule wanda ya rasu yau.
Gwamnatin jihar kano ta bada hutun ƙwana daya don rasuwar Dan masani kano
Gwamnatin ta bada hutun a wani bayani da ƙwamishnan labarai Mallam Muhammed Garba ya fitar.
An bada hutun a wata sanarwa da ƙwamishnan labarai Mallam Muhammed Garba ya bayyanar tare da sa hannu.
Cikin bayanin, “ munji labarin rasuwar Alhaji (Dr) Yusuf Maitama Sule Dan masanin Kano yau litinin 3 ga watan Yuli.
“Maitama Sule ya rasu a kasar masar inda yake jinyar wata ciwo da yake fama da ita.
“Za’ayi jana’izar sa gobe talata 4 ga watan Yuli a fadar sarkin kano, kofar kudu da karfe 4:00 na yamma.”
“Gwamnan jihar Kano bada hutu na ƙwana daya don jimamin wani babban rashi da jihar kano tayi.”
A bayani da jaridar Punch ta fitar, babban dan shi Alhaji mukhtar Maitama Sule ya ayyana cewa ya rasu sa’o’i 24 da isowar sa asibiti.
Gawar shi zata iso nijeriya gobe don ƙaddamar da jana’iza
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng