ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Gwamnatin jihar Jigawa ta bada hutun kwana daya don yi wa shugaba Buhari addu’a

Gwamnatin ta bada hutun don ma’aikata da sauran yan jihar su taimaka wajen yi wa shugaba Buhari addu’a ta mussamman na samun lafiya.

President Muhammadu Buhari

Gwamnatin jihar jigawa ta ƙaddamar da ranar juma’a 7 ga watan Yuli a matsayin ranar hutu don ma’aikata su taimaka wajen yi wa shugaba addu’a na samun lafiya cikin gaggawa

Jami’in hulda da jama’a na huƙumar ma’aikata na jihar Alhaji Isma'il Ibrahim ya sanar da haka a wata bayani da ya fitar ranar al’hamis a garin Dutse.

Ibrahim yace fadar gwamnatin ta yanke shawarar bada hutun bayan wata zama da tayi ranar 5 ga watan Yuli

Yace gwamantin ta ƙaddamar da ranar juma’a a matsayin ranar hutu don ma’aikata da sauran mutane jihar su taimaka wajen yi shugaba Buhari addu’a na sauki daga rashin lafiya da yake fama da ita.

ADVERTISEMENT

“A wannan ranar na hutun ana sa ran cewa ma’aikatan da sauran al’ummar jihar zasu taimaka don yi wa shugaban mu addu’a na Allah ya bashi lafiya cikin gaggawa” yace.

“Kuma muna fatan zasu yi wa Dan masanin Kano Alhaji Yusuf Maitama Sule addu’a  Allah yasa Aljanna ce makomarsa”  ya kara.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT