Dakarun sojoji dake yaki da yan boko haram sun ƙashe wasu da ake zargin cewa yan darikar boko haram ne a ƙauyen mussini na jihar Borno.
Dakarun sojoji sun ƙashe yan ta’adda biyar a jihar Borno
An harbi yan darikar boko haram yayin da suke neman yin satar kayan abinci a wani ƙauye
An harbi yan ta’addar yayin da suke neman satar kayan abinci daga kauyen
Shafin Daily sun ruwaito cewa, bataliya 3 na birged 22 suka yi kwantan bauna harbin su yayin da aka sanar da zuwan yan ta’adda
Jami’in hulda da jama’a na rundunar sojoji brig.gen Sani Usman a bayanin shi yace,” mun gano wasu makamai daga yan ta’addar, aciki akwai bindigar AK 47, mujallar AK 47, harsassai, kekuna 27, adduna 10 da wuka daya.”
Wannan ya faru bayan wasu mata yan ƙonar bakin wake suka tada kansu da bam yayin da wasu yan banga suka gano su a wani gari mararrabar jihar da kamaru.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng